Yadda jami’an tsaro suka tsaurara tsaro a gidan gwamnatin Kano

Date:

  1. Daga Aliyu Danbala Gwarzo

 

Jami’an tsaro da suka hadar da hadakar dukkanin jami’an daga hukumomin tsaro Nigeria sun tsaurara matakai a birnin kano, yayin da ake jiransa hukuncin Kotun Ƙoli kan shari’ar zaɓen gwamnan jihar kano.

 

Wakilin kadaura24 ta bamu labarin cewa an jibge tarin jami’an tsaro a kofar shiga gidan gwamnatin jihar kano domin tabbatar da tsaro a gidan.

Da dumi-dumi: Kotun Ƙoli ta Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan Lagos

A wasu daga cikin titunan birnin ma an jibge tain jami’an tsaro domin shirin ko ta kwana bayan kammala yanke hukuncin Kotun Ƙoli Ƙoli zata yi nan da wani lokaci kankani.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito kwamishinan yan sandan jihar kano CP Husaini Gumel ya sha alwashin daukar matakan ba sani ba sabo a kan duk wanda ya karya doka bayan kotun kolin ta yanke hukunci kan shari’ar zaɓen gwamnan jihar.

Tarihin Alƙalin Da Zai Jagoranci Yanke Hukuncin Shari’ar Zaɓen Gwamnan Kano

Jama’a da dama sun zauna a gidajen su don gudun abun da ka je ya zo bayan hukuncin, duk kuwa da yadda hadar jami’an tsaro ke sintiri a titunan birnin kano domin tabbatar da kare rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-yanzu: Naja’atu Muhd ta mayarwa da Nuhu Ribado Martani Kan barazanar da ya yi mata

Daga Isa Ahmad Getso   Yar gwagwarmayar nan Hajiya Naja'atu Muhammad...

Zargin Sharrin: Ribado ya yi barazanar maka Naja Muhammad a Kotu

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Mai baiwa shugaban kasa shawara kan...

Rusau: Kwankwaso ya bukaci gwamnan Kano ya biya diyyar mutanen da aka kashe a Rimin Zakara

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jigon jam’iyyar APC a jihar Kano,...

Za mu karawa Limamai, Ladanai da Na’ibansu alawus na wata-wata – Shugaban Karamar hukumar Dala

Daga Sani Idris maiwaya   Shugaban karamar hukumar Dala Alhaji Suraj...