MatsalarTsaro :Gwamnatin jihar Kano ta bada Umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda

Date:

 Daga Nasiba Rabi’u Yusuf


 Gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda ba tare da bata lokaci ba.


  Kwamishinan Ilimi na jihar, Malam Muhammad Sanusi Sa’id Kiru ya sanar da cewa rufe kwalejin ya zama tilas biyo bayan wani rahoton tsaro da gwamnati ta samu da kuma bukatar kare rayukan dalibai, malamai da sauran ma’aikatan kwalejin.


 Cikin Wata sanarwa da Jami’in Hulda da jama’a na Ma’aikatar Ilimi Aliyu Yusuf ya aikowa Kadaura24 yace Kwamishinan ya bukaci iyaye da su hanzarta kwashe yaransu daga Kwalejin kuma su jira karin umarnin.


 Kwamishinan yayi amfani da damar don nuna godiyar gwamnatin jihar ga iyaye bisa goyan baya da hadin kai kan manufofi da umarnin gwamnati musamman kan al’amuran da suka shafi tsaro.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Nijeriya ta yi babban rashi: Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Aminu Dantata

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya...

Rasuwar Alhaji Aminu Dantata ta bar gibin da zai yi wuyar cikewa a Nigeria – Alhaji. Kabiru Sani Kwangila

Shugaban kamfanin gine-gine na SKY Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Sanarwa ta Musamman daga majalisar malaman Kano game da rasuwar Dantata

SANARWA MUHIMMIYA (GABATAR DA SALLATUL GA'IB) Assalamu Alaikum Warahmatullah, Sakamakon rasuwa...

Aminu Dantata ya bar mana wasiyyar inda za a binne shi – Iyalansa

Iyalan marigayi Alhaji Aminu Alassan Dantata sun shaida cewa...