MatsalarTsaro :Gwamnatin jihar Kano ta bada Umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda

Date:

 Daga Nasiba Rabi’u Yusuf


 Gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda ba tare da bata lokaci ba.


  Kwamishinan Ilimi na jihar, Malam Muhammad Sanusi Sa’id Kiru ya sanar da cewa rufe kwalejin ya zama tilas biyo bayan wani rahoton tsaro da gwamnati ta samu da kuma bukatar kare rayukan dalibai, malamai da sauran ma’aikatan kwalejin.


 Cikin Wata sanarwa da Jami’in Hulda da jama’a na Ma’aikatar Ilimi Aliyu Yusuf ya aikowa Kadaura24 yace Kwamishinan ya bukaci iyaye da su hanzarta kwashe yaransu daga Kwalejin kuma su jira karin umarnin.


 Kwamishinan yayi amfani da damar don nuna godiyar gwamnatin jihar ga iyaye bisa goyan baya da hadin kai kan manufofi da umarnin gwamnati musamman kan al’amuran da suka shafi tsaro.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...