MatsalarTsaro :Gwamnatin jihar Kano ta bada Umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda

Date:

 Daga Nasiba Rabi’u Yusuf


 Gwamnatin jihar Kano ta bada umarnin rufe Kwalejin Fasaha ta Bagauda ba tare da bata lokaci ba.


  Kwamishinan Ilimi na jihar, Malam Muhammad Sanusi Sa’id Kiru ya sanar da cewa rufe kwalejin ya zama tilas biyo bayan wani rahoton tsaro da gwamnati ta samu da kuma bukatar kare rayukan dalibai, malamai da sauran ma’aikatan kwalejin.


 Cikin Wata sanarwa da Jami’in Hulda da jama’a na Ma’aikatar Ilimi Aliyu Yusuf ya aikowa Kadaura24 yace Kwamishinan ya bukaci iyaye da su hanzarta kwashe yaransu daga Kwalejin kuma su jira karin umarnin.


 Kwamishinan yayi amfani da damar don nuna godiyar gwamnatin jihar ga iyaye bisa goyan baya da hadin kai kan manufofi da umarnin gwamnati musamman kan al’amuran da suka shafi tsaro.

15 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...