Kungiyar kwadago NLC ta sanar da ranar da zata tsunduma yajin aikin gargaɗi

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta sanar da cewa zata tsunduma yajin aikin gargadi na kwanaki 2, daga ranar Talata 5 gawatan Satumba zuwa Laraba.

 

Kungiyar tace zata yi haka ne saboda batun cire tallafin man fetur da ya jefa al’ummar kasar nan cikin matsin rayuwa.

Talla

Shugaban kungiyar kwadago ta NLC Joe Ajaero ne ya sanar da haka a yau juma’a, a wani taron manema labarai da ya gudana a shalkwatar kungiyar dake Abuja.

 

Kungiyar kwadagon ta zargi gwamnatin tarayya da watsi da cigaba da tattaunawa da ita, da kuma rashin cika alkawurran da gwamnatin tarayya tayi musu a yayin ganawar da sukayi a baya-bayan nan.

Dashen bishiyoyi ne kadai zai magance matsalar dumamar yanayi a cikin al’umma – Sarkin Bichi

Wannan mataki ya biyo bayan zanga-zanga da kungiyar kwadagon ta yi a ranar 2 ga watan Agustan da ya gabata, duk dai kan batun tsadar rayuwar da cire tallafin man fetur ya jefa yan kasar nan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Murtala Sule Garo Ya Taya Al’ummar Musulmi Barka da Shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447AH

    Tsohon dan takarar mataimakin gwamnan jihar Kano, Alhaji Murtala...

Tinubu zai mayar da Fubara kan kujera gwamnan Rivers amma ya gindaya masa sharadi- Rahoto

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da mayar...

Yadda Makarantar JSS Unguwa uku dake K/H Tarauni ta Zama mafakar shaye-shaye da yan daba

Daga Mubina Ahmad Galadanchi Wasu daga cikin al'ummar unguwar unguwa...

Hukumar almajirai da yaran da ba sa zuwa Makaranta ta kaddamar da yi wa yaran da ba sa zuwa Makaranta Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...