Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Kungiyar kwadago ta kasa NLC ta sanar da cewa zata tsunduma yajin aikin gargadi na kwanaki 2, daga ranar Talata 5 gawatan Satumba zuwa Laraba.
Kungiyar tace zata yi haka ne saboda batun cire tallafin man fetur da ya jefa al’ummar kasar nan cikin matsin rayuwa.

Shugaban kungiyar kwadago ta NLC Joe Ajaero ne ya sanar da haka a yau juma’a, a wani taron manema labarai da ya gudana a shalkwatar kungiyar dake Abuja.
Kungiyar kwadagon ta zargi gwamnatin tarayya da watsi da cigaba da tattaunawa da ita, da kuma rashin cika alkawurran da gwamnatin tarayya tayi musu a yayin ganawar da sukayi a baya-bayan nan.
Dashen bishiyoyi ne kadai zai magance matsalar dumamar yanayi a cikin al’umma – Sarkin Bichi
Wannan mataki ya biyo bayan zanga-zanga da kungiyar kwadagon ta yi a ranar 2 ga watan Agustan da ya gabata, duk dai kan batun tsadar rayuwar da cire tallafin man fetur ya jefa yan kasar nan.