Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa
Kwamitin amintattu (BoT) na jam’iyyar NNPP mai alamar kayan marmari sun sanar da dakatar da Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso na tsawon watanni shida saboda zarginsa da yiwa jam’iyyar zagon kasa a zaben daya gabata.
Kwamitin amintattun sun fitar da sanarwar dakatarwar ta Kwankwaso a ranar Talata, 29 ga watan Agusta kamar yadda aka wallafa a shafin TVC News.

Kwamitin amintattun dai ya ce ya ɗauki wannan matakin kan Kwankwaso ne saboda zarginsa da cin amanar jam’iyyar ta hanyar yiwa jam’iyyar APC aiki a zaben shekara ta 2023.
Gwamnatin Kano ta musanta kin tantance wasu daga cikin ma’aikatan da Ganduje ya ɗauka
Rikici dai ya barke a jam’iyyar bayan dakatarwar da aka yiwa dan takararta na shugaban kasa kuma jagoran ta na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
Hakan ya biyo bayan dakatarwar da sakataren yada labaranta na kasa da wasu suka yi a baya, matakin da kwamitin amintattu ya yi watsi da shi.