Juyin Mulkin Nijar: Muhammad Bazoum ya bayyana halin da ya shiga a hannun sojojin Nijar

Date:

Daga Maryam Ibrahim Muhammad

 

Hambararren shugaban Jamhuriyar Nijar, Mohamed Bazoum, ya ce an killace shi tare da tilasta masa cin busasshiyar shinkafa.

 

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a ranar 26 ga Yuli, 2023, sojojin Nijar suka hambarar da Bazoum tare da dakatar da kundin tsarin mulkin kasar.

Da dumi-dumi: Tinubu na ganawa da El-Rufai da Wike a fadar shugaban kasa

Shugaba Bola Tinubu, wanda shi ne Shugaban Kungiyar bunkasa Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS), ya shirya wani taro a yau Alhamis bayan wa’adin kwanaki 7 da kungiyar ta fitar na maido da Shugaba Mohamed Bazoum kan mukaminsa ya cika.

Talla

Tashar talabijin ta CNN ta ruwaito Bazoum a cikin jerin sakonnin tes da ya aike wa wani abokinsa yana cewa “an hana shi hulda da mutane” tun daga ranar Juma’a, ba tare da an kai masa abinci ko magunguna ba.

 

A cewar hambararren shugaban, ya shafe mako guda yana rayuwa a Ina babu hasken wutar lantarki, al’amarin da ya zama ruwan dare ga daukacin ‘yan Nijar bayan da Najeriya ta katse wutar lantarki sakamakon juyin mulkin.

Bazoum ya ce duk abincin da aka kawo masa ya lalace, kuma yanzu yana cin busasshiyar taliya da shinkafa.

Da dumi-dumi: Ganduje ya baiwa tsohon kwamishinansa mukami

Duk da keɓantace shi, Bazoum yana samun goyon bayan ƙasashen duniyar .

Ko da yake an ki bashi damar tattaunawa da mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka Victoria Nuland a ziyarar da ta kai Yamai babban birnin Nijar a ranar Litinin, Bazoum ta tattauna da sakataren harkokin wajen Amurka Antony Blinken ta wayar tarho.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...