Yanzu-Yanzu :Yan Sanda a Zamfara sun kubutar da Dalibai 2 Cikin Daliban da aka sace a Yauri

Date:

Daga AB Kaura

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta ceto dalibai biyu daga cikin daliban da aka sace na kwalejin Birnin Yauri a jihar Kebbi.

Kadaura24 ta rawaito Kwamishinan ‘yan sanda na rundunar,CP Hussaini Rabiu ya baiyana haka yayin ganawarsa da manema labarai a hedikwatar’ yan sanda da ke Gusau ya ce an ceto daliban ne a kauyen Babbar Doka da ke gundumar Dansadau a karamar hukumar Maru a jihar Zamfara.

“Ma’aikatan mu na Operation zaman lafiya sun yi nasarar kubutar da dalibai biyu wato Maryam Abdulkareem ‘yar shekara 15 a karamar hukumar Wishishi ta jihar Neja da Faruk Buhari dan shekara 17 na karamar hukumar Wara ta jihar Kebbi lafiya a Kauyen Doka a gundumar Dansadau ”inji CP Hussaini .

Kwamishinan ya yi bayanin cewa, an kai daliban asibiti domin duba lafiyarsu kuma ‘yan sanda suna kara samun bayanai Daga Daliban.

Lura da cewa, za a mika daliban ga rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi don ci gaba da daukar matakan da suka dace tare da mika su ga Iyayen su.

Wasu daga Cikin yan uwan daliban da aka sako wadanda suka halarci taron manema labaran sun nuna farin ciki tare da nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki da Kuma kokarin ‘Yan Sandan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sallah: Baffa Babba ya raba buhu 2,000 na Shinkafa ga Kungiyoyin Tinubu a Kano

Babban daraktan cibiyar kula da ingantuwar aiyuka ta kasa...

Babbar Sallah : Kansilan Lajawa ya raba Naira dubu 500 ga al’ummar mazabarsa

Daga Nura Adam   Kansilan mazabar Lajawa a karamar hukumar Wudil...

Da dumi-dumi: Kotu ta aike da Matashin dake shigar mata a Tiktok da film gidan gyari

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Shugaban Hukumar tace fina-finai da Dab'i...

Rabon Jakai: Faizu Alfindiki ya aikawa Sanusi Bature budaddiyar wasika

Zuwa ga: DG. Sunusi Bature Dawakin Tofa Daraktan Yada Labarai, Gwamnatin...