Gwamnatin Kano ta bayyana dalilin Sanya hoton Muhd Sanusi II a dakin taro na Coronation

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

 

Zauren Coronation mai dimbin tarihi da ke fadar gwamnatin jihar Kano, yana da mahimmaci na musamman a cikin abubuwan tarihi na birnin domin tun da farko an gina shi ne domin nadin sarautar Sarkin Kano na 14, Malam Muhammadu Sanusi.

 

Zauren wanda a cikin sa aka mika shaidar kama aiki ga Muhammad Sanusi II bayan ya gaji marigayi Alhaji Ado Bayero a shekarar 2014 a lokacin gwamnatin Sen. Rabi’u Musa Kwankwaso, yanzu haka ana ci gaba da gyare-gyare domin dawo da martabar dakin taron dake fadar gwamnatin jihar kano.

Talla

Wani muhimmin abu na wannan aikin na gyare-gyare shi ne mayar da hoton Sarki na 14, Malam Muhammadu Sanusi, a cikin zauren. Kamar yadda aka saba, hoton zai kasance a can har abada, don tunawa da dalilin samar da dakin taron.

Da dumi-dumi: Tinubu zai yi jawabi ga al’ummar Nigeria

Gyaran da ake ci gaba da yi na nufin yi zauren Coronation gyaran fuska da ake bukata, tare da kiyaye muhimmancin tarihi da al’adunsa.

Sanusi Bature Dawakin Tofa, Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamnan Jihar Kano, ya tabbatar da cewa gyaran zauren ya hadar da dawo da hoton Sarkin na 14.

Zauren taro na Coronation yana da kima sosai ga al’ummar Kano, kuma gyaran da aka yi masa na nuna aniyar gwamnatin na kiyaye dimbin tarihi da al’adun gargajiya na mutanen Kano.

A safiyar wannan rana ce dai aka wayi gari da hotunan na tsohon Sarkin kano Muhammad Sanusi II, wanda ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...