Wajibi ne Sanya Kafar Wando Guda da Masu Dabi’ar Shaye_shaye a Cikin al’ummarmu – Sarkin Kano

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya sha alwashin hada karfi da gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki domin dakile mummunar dabi’ar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.

 

Mai Martaba Sarkin ya bayyana hakan yayin taron wayar da kan matasa wanda kungiyar INITIATIVE FOR COMMUNITY ACTION AGAINST DRUG ABUSE ( ICAADA ) wadda ke yaki da dabi’ar shaye-shaye ta dauki nauyin taron a jami’ar Yusuf Maitama sule dake kano.

Talla

Alhaji Aminu Ado Bayero ya ja hankali jami’an tsaro dasu kara lura da yadda matasa suke safara da shan kayan maye wadanda suke sadiyyar lalacewar rayuwar su da kuma kawo cikas ga cigaban su da jihar kano baki daya.

Shuwagabannin APC Na Arewa Maso Yamma Sun Amince Da Ganduje A Matsayin Shugaban Jam’iyyar Na Kasa

Ya yi kira ga dukkanin shugabannin al’umma da su kansu al’ummar da su maida hankali wajen ganin an cigaba da wayar da kan al’ummar musamman matasa illolin shan miyagun kwayoyi.

Sojoji sun bayyana dalilan da suka sa suka yi juyin mulki a Nijar

Shi ma anasa bangaran Ahmad Abubakar yakasai yaja hankalin dalibai da su guji yin abota da abokanai masu tu’ammali da muggan kwayoyi, sannan su rika jan hankali abokansu da suke yi don su gujewa dabi’ar saboda yadda take lalata rayuwar matasa .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...