Da dumi-dumi: Jami’an tsaro sun tsare shugaban Niger

Date:

Daga Halima Musa Sabaru

 

Jami’an tsaron fadar shugaban kasar na tsare da Mohamed Bazoum, shugaban kasar Nijar, bayan da ya sojojin Kasar suka bukaci ya sauka kamar yadda wata majiya kusa da Bazoum ta ruwaito a ranar Laraba.

 

Wasu daga cikin masu gadin da suka fusata sun rufe hanyar shiga gidan shugaban da ofisoshinsu, kuma bayan da tattaunawar ta kaure “sun ki sakin shugaban,” majiyar ta kara da cewa: “Sojoji sun ba su wa’adi .”

Talla

A wani sako da aka fitar a shafin Twitter, wanda ake yiwa lakabi da X, ofishin shugaban kasar ya ce “bangaren dakarun tsaron fadar shugaban kasa sun yi fushi, don haka sun shirya daukar mataki akan duk wasu son kai tarnaki kasar .”

Yadda Kansiloli suka dakatar da shugaban karamar hukuma a Kano

Sojoji da jami’an tsaron kasa a shirye suke su kai farmaki kan ‘yan ta’addar PG da ke da hannu a cikin wannan hali da ƙasar take ciki ,” inji fadar shugaban kasar.

“Shugaban da danginsa suna cikin koshin lafiya,” in ji shi.

An zabi Bazoum ta hanyar dimokiradiyya a shekarar 2021, inda ya karbi ragamar shugabancin kasar da take cikin kasashe mafi talauci a Afirka .

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...