Wasan taya Murnar Karin Girma: Mazauna gidan Yari na kurmawa sun lallasa Ma’aikatan gidan gyaran hali

Date:

Daga Abdullahi Shu’aibu Hayewa

 

Kungiyar Kwallon Kafa ta Gidan gyaran Hali ta kasa Reshen Jihar Kano wato FC Kano Correctional Tigers ta fafata wasa tsakaninta da mazauna Gidan gyaran Hali na Kurmawa a jiya Juma’a.

 

A yayin wasan mazauna gidan gyaran halin dake kurmawa sun lallasa Kungiyar Ma’aikatan gidan gyaran halin reshen jihar Kano daci 7-6 .

Yadda Kamfanin UK ENTERTAINMENT Ya Shirya Sabon Fim Mai Dogon Zango Mai suna FATAKE

Wasan dai shi ne irinsa na Farko da aka gudanar dan taya murnar karin girma ga ma’aikatan gidan gyaran halin reshen Jihar Kano.

Tallah

Kadaura24 ta rawaito ma’aikatan gidan gyaran hali reshen jihar Kano Sama Dubu daya ne suka samu karin girma a matakai daban-daban.

A karshe Kaftin din Kungiyar Kwallon Kafar ta Gidan gyaran hali reshen jihar Kano, Inspector Abbas Abubakar Musa ya yabawa yan wasan sa bisa namiji kokarin da su kayi a yayin wasan da su ka buga tsakaninsu da mazauna Gidan gyaran Halin dake Kurmawa.

 

Sanann ya yabawa suma mazauna gidan gyaran halin dake kurmawa bisa yadda suka buga wasan cikin farin ciki da annushuwa, kuma har suka taya ma’aikatan murnar karin girman.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...