Daga Khadija Abdullahi Aliyu
Shugaban ƙasar Najeriya Bola Tinubu ya amince da cewa Najeriya na fuskantar kalubale mai tarin yawa, amma kuma a cewarsa yana kokarin samar da hanyoyin magance matsalolin.
A cikin sanarwar da ya fitar na taya musulmin Najeriya murnar Barka da Sallah, Asiwaju Tinubu ya ce “Dole ne mu gode wa Allah Madaukakin Sarki da ya ba mu damar halartar wata Sallar Idi”.

Ya ƙara da cewa Allah ba ya ɗora wa mutum abin da ba zai iya ɗauka ba.”
“Allah Ya san halin da ƴan Najeriya ke ciki kuma zai kawo musu sauƙi.”
Jerin gwanon motocin Tinubu ya haifar da cece-kuce a Nigeria
Sannan ya buƙaci al’umma da su yarda cewa ƙasar za ta gyaru, su kuma haɗa hannu wajen cimma nasarar hakan.
Ya kara da cewa gwamnatinsa ta fara neman hanyar magance matsalolin da ke addabar kasar, ta hanyar shawarwarin da suke samu daga wajen kwararru don gyara tattalin arziƙi da kuma kawarda duk wani cikas da zai hana bunƙasar Najeriya.