Da dumi-dumi: Abba Gida-gida ya Magantu kan baiwa dansa mukami

Date:

Daga Sani Idris Maiwaya

 

Gwamnan Jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya musanta labarin da ake yadawa cewa ya nada dansa a matsayin Sakataren zartarwar na hukumar Adana tarihi da al’adu ta jiha .

 

Idan za’a iya tunawa wasu jaridu sun rawaito Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya naɗa ɗansa na riƙo, Ahmad A. Yusuf a matsayin Sakataren zartarwar na Hukumar Tarihi da Al’adu ta jihar.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya tura sunayen wadanda zai nada a matsayin kwamishinoni

Rahotan dai ya bayyana cewa Ahmad A. Yusuf ɗa ne ga shaƙiƙin gwamnan, amma a hannunsa ya taso har ma ake masa kallon ɗansa na fari.

Da dumi-dumi: Shekarau ya Magantu kan gayyatar da Majalisar Dinkin duniya ta yi masa

A wata sanarwa da babban Sakataren yada labaran Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, yace Art. Ahmad Abba Yusuf da ne ga Sakataren Masarautar kano Alhaji Abba Yusuf.

Idan za a iya tunawa dai, lokacin da gwamnan ke karɓar satifiket na nasarar zaɓensa daga hukumar zaɓe, INEC ranar 29 ga Maris, 2023, gwamnan ya bada tabbacin cewa ba zai sa iyalinsa cikin harkokin mulki ba.

Babu yadda za a yi in bar iyalina su tsoma baki a harkokin gwamnati ba, saboda ni kaɗai na rantse ba tare da su ba, wato dai su babu su a gwamnati,’” in ji Gwamnan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...