Da dumi-dumi: Shekarau ya Magantu kan gayyatar da Majalisar Dinkin duniya ta yi masa

Date:

Daga Aliyu Danbala Gwarzo

Tsohon gwamnan Kano kuma tsohon sanatan Kano ta tsakiya Malam Ibrahim Shekarau, ya ce ya samu wani goron gayyata na musamman daga sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya zuwa birnin New York dake Amurka.

 

Kadaura24 ta rawaito Malam Shekarau wanda shi ne Sardaunan kano yace da Gaske ne majalisar ta gayyace shi, amma ba’a yi masa cikakken bayani kan dalilin gayyatar ba, amma zai amsa gayyatar a mako mai zuwa.

Yanzu-Yanzu: Abba Gida-gida ya tura sunayen wadanda zai nada a matsayin kwamishinoni

A wani sako da mai taimakawa tsohon gwamnan kan kafafen sada zumunta da daukar hoto Jibril Muhammad Na-Tara ya wallafa ya tabbatar da wannan goron gayyata da aka aikewa tsohon gwamnan na Kano Malam Ibrahim Shekarau.

Tallah

Yanzu dai abun jira shi ne aji menene dalilin gaiyatar da majalisar dinkin duniyar ta yiwa Malam Ibrahim Shekarau, wata kila idan ya dawo ya yiwa al’umma bayani gane da abubun da suka tattaunawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...