Yanzu-Yanzu: Saudiyya ta bayyana ranar da za’a yi Arfa da Babbar Sallah

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hukumomi a Kasar Saudiyya sun bayyana cewa an ga jinjirin watan Zulhajj a kasar a wannan rana ta Lahadi, wanda hakan yasa gobe litinin ya zama daya ga watan Zulhajj.

 

Sanarwar da sashin Haraimain Sharifain ya fita da yammacin wannan rana ta Lahadi, sun nuna cewa za’a gudanar da hawan arfa a ranar talata 27 ga watan Yuni 2023, wanda yayin dai-dai da 9 ga watan Zulhajj 1444 bayan Hijira.

KEDCO sun bayyana dalilin da yasa ake fuskanta rashin wuta a Kano, Jigawa da Kaduna

Sanarwar ta Kuma Kara da cewa Babbar Sallah zata kasance ranar Laraba 10 ga watan Zulhajj dai-dai da 28 ga watan Yuni na shekarar 2023.

Tallah

Idan za’a iya tunawa kadaura24 ta rawaito a jiya asabar hukumomin ƙasar saudiyya suka bada sanarwar fara duba jinjirin watan na Zulhajj a wannan rana ta Lahadi kamar yadda Nigeria ma ta bada umarnin fara duban watan ta bakin Sarkin Musulmi Alhaji Muhammad Sa’eed Abubakar na 3.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...