Abduljabar: Matakin da Ganduje ya Dauka Kan Abduljabar abun yabo ne – Kungiyar JNI

Date:

Kungiyar Agaji Tara kasa reshen jahar Kano ta yabawa Gwamnatin jahar Kano bisa girmama addinin musulunci da malamai da takeye.

Shugaban kungiyar na jahar Kano Muhd Nuruddeen Lawan Gwagwarwa ne ya baiyana haka a sakonsa na barka da sallah ga al’ummar musulmi.

Yace gwamnatin jihar Kano tayi abun a yaba Mata Saboda da Matakin data dauka akan Wani Malami da yasu Kawo rudani da raba Kan mabiya addinin Musulunci.

Yace Yana Taya daukacin al’ummar musulmi Kano Dana Nigeria Baki daya Murnar zagayowar idin Babbar Sallah, Inda ya bukaci al’umma su cigaba da yin koyi da aiyukan alkhairin da Suka gabatar a kwanaki 10 Farko na Watan zulhijja.

Alhaji Nuruddeen Gwagwarwa ya Kuma yabawa malamai bisa addu’o’i da ilimantarwa da wayar dakan al’umma da suke akoyaushe, Sannan yayi kira ga al’ummar musulmi dasu kasance masu bin tsarin shari’ar musulunci a dukkan lamuransu na yau da kullun.

Shugaban Kungiyar ya Kuma yi kira ga Malamai a jihar nan dasu karfafa tsarin hadinkai, fahimtar juna da zaman lafiya a tsakanin alumma’a. A kashe ya Kuma yi kira ga al’umma dasu cigaba da adu’o’in samun zaman lafiya Mai dorewa a Kano da Kasa baki daya

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...