Marayu 100 a kano sun rabauta da Tallafin Naman Sallah daga Falakin Shinkafi

Date:

 

Kimanin Marayu 100 sun Amfana da tallafin Naman Sallah da Barka da Sallah a unguwar Yakasai Daga Wani Dan Kasuwa Kuma Dan kishin Kasa Ambasada Yunusa Yusuf Hamza ( Falakin Shinkafi).

Da yake Zantawa da Wakilin Kadaura24 Jim kadan bayan kammala rabon Falakin Shinkafin Amb. Yunusa Yusuf yace ya tallafawa marayun ne domin Sanya farin Ciki a zukatansu a Wannan Lokaci na Sallah Babba.

Yace Marayu Suma’ya’yane da ya kamata a Rika kula dasu Musamman a Lokaci irin Wannan domin a dauke musu radadin Rashin Iyayen su.

Amb. Yunusa Yusuf yace ya Zama wajibi mawadata su Rika tallafawa marayu don kyautata Rayuwar su, “Idan ba’a taimaki Rayuwar su ba hakan ce take sawa su taso basa tausayi Kuma su zamo gurbatattu Saboda da Suma ba’a taimaki Rayuwar suba.

” Ina Amfani da Wannan dama wajen Kira ga Shugabanni da mawadata dasu Rika tallafawa marayu don inganta Rayuwar tare da Samun lada Mai yawa a wajen Allah”. Inji Falakin Shinkafin

Wasu Daga Cikin Iyayen Marayun da Suka Amfana da tallafin sun yabawa Ambassador Yunusa Yusuf Hamza (Falakin Shinkafin) bisa tallafin da ya Baiwa ya’yansu, Inda Suka ce dama ya saba gudanar da irin Wannan tallafi ta karkashin Kungiyar Yakasai Zumunta.

Kadaura24 ta rawaito bayan Naman Sallah Marayun sun rabauta da kudi da Kayan more Rayuwa don faranta musu a Wannan Lokaci na Sallah.

98 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...