Rasuwar Mahaifiya ga Sarakunan Kano da Bichi, Babban Rashi ne ga Kasa- Garban Kauye

Date:

Daga Surayya Abdullahi Tukuntawa

Shugaban karamar Hukumar Kumbotso Hon Hassan Garban Kauye Farawa ya Bayyana Rasuwar Hajiya Maryam Ado Bayero ( Mama Ode ) Mahaifiyya ga Sarkin Kano Alh Aminu Ado Bayero Dana Bichi Alh Nasir Ado Bayero amatsayin Babban Rashi ga Kasar Nan Baki Daya Ba iya jihar Kano ba.

Shugaban karamar Hukumar ta Kumbotso Alh Hassan Garba Amadadin Al’ummar karamar hukumar ta Kumbotso na Mika Sakon Ta’azziya ga Masarautar Kano Da Bichi da Kuma Mai girma gwamnan jihar Kano Dr AU Ganduje, Shugaban jam’iyar APC Hon Abdullahi Abbas Sunusi, kwamishinan kananan Hukumomi Hon Murtala Sule Garo da Daukacin Al’ummar jihar Kano. da fatan Allah Swt ya Kai Rahama kabarinta.

” Innalillahi wa innailahir raji’un Allah Daya Dauketa yafimu Sonta, Allah ya Bata Albarkacin Wannan wata na Ramadan ya garfarta Mata” a cewarsa Cikin Sakon Ta’azziyar Daya wallafa, Dauke Dasa Hannun Mai Taimakamasa na musamman Kan Harkokin yada labarai Shazali farawa.

Kazalika shugaban karamar hukumar Kumbotso Amadadin ma’aikatan karamar hukumar ya Mika sakon ta’aziyya ga Darakatar Mulki ta karamar Hukumar Kumbotso Hajiya Umma Abbas Sunusi Wakiliyar Galadiman Kano da fatan Allah Swt ya kyautata makwanci.

A karshe yayi fatan Allah ya baiwa iyalai da Al’ummar jihar Kano Dama kasa Baki Daya Hakurin jure wannan Babban Rashi.

93 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...

Da dumi-dumi: Tinubu ya nada sabon Minista

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya aike da sunan...

Kashim Shattima ya sauka daga kujerar ta mataimakin shugaban Nigeria ya baiwa wata yarinya

Mataimakin shugaban Kasa Kashim Shattima ya sauka daga kujerarsa...