Kotun sauraren kararrakin zaben shugaba ta bada tabbacin yi wa kowa adalci

Date:

Daga Safiyanu Dantala Jobawa

 

Kotun sauraron ƙorafe-ƙorafe kan zaɓen shugaban kasa ta fara zama a yau Litinin.

 

An fara zaman ne da misalin ƙarfe 9:15 na safe, inda alƙalin da ke jagorantar zaman kotun, mai shari’a Haruna Tsammani ya gabatar da jawabi.

Tsammani ya ce kotun za ta yi masu ƙarar adalci sannan ya gargaɗi lauyoyi da su guje wa yin kalamai na harzuƙawa.

Bankwana: Ganduje ya yafewa malaman makaranta kudaden gidaje

Ya kuma buƙace su da su bai wa kotun haɗin kai domin ganin an kammala shari’ar cikin lokacin da aka ɗiba.

 

Sauran alƙalan da za su taimaka wajen gudanar da shari’ar sun haɗa da mai shari’a Stephen Adah da Misitura Bolaji-Yusu da Boloukuoromo Moses Ugo da kuma Abbah Mohammed.

 

Gabanin fara zaman, an jibge jami’an tsaro a kan hanyoyin da suke kai wa zuwa kotun.

 

Jam’iyyun adawa irin su PDP da LP ne suka shigar da ƙara suna ƙalubalantar nasarar da ɗan takarar jam’iyyar APC mai mulki, Bola Tinubu ya samu a zaɓen shugaban ƙasa na 2023.

 

Kadaura24 ta rawaito Sakamakon da INEC ta fitar ya nuna cewa Bola Tinubu na APC ya samu ƙuri’u 8,794,726, sai Atiku Abubuakar na jam’iyyar PDP wanda ya samu ƙuri’a 6,984,520, yayin da Peter Obi na jam’iyyar LP ke biye masu da ƙuri’a 6,101,533.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi: Gwamnan Kano ya tura tawaga mai karfi wajen Abba Ganduje

Daga Rahama Umar Kwaru   Babban Daraktan Hukumar Samar da Wutar...

Wata sabuwa: Sanata Barau Jibrin ya gana da Baffa Bichi da Muhd Diggol

Tsohon sakataren gwamnatin Jihar Kano Dakta Abdullahi Baffa Bichi...

Rikicin Masarautar Kano: Kotu ta Sake Sabon Hukunci

A wani sabon yanayi na rikicin Masarautar Kano, Kotun...

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...