Rashin Mai Babban Daki Zai bar gibi Mai yawa a Kano – Alhassan Ado Doguwa

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Wakilai ta Kasa Kuma Dan Majalisa Mai Wakiltar Kananan Hukumomin Tudun Wada da Doguwa Hon. Alhassan Ado Doguwa ya aike da sakon ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyar Masu Martaba Sarakunan Kano da Bichi ga iyalanta da al’ummar jihar Kano baki Daya.

Cikin Wata sanarwa Mai dauke da sa hannun Mataimaki na musamman ga Shugaban Majalisar Wakilai Auwal Ali Sufi utai ya aikowa Kadaura24 ya bayyana Rasuwar Hajiya Maryam Ado Bayero a Matsayin babban Rashi ba ga ga iyalanta kadai ba har da al’ummar jihar Kano Dana Kasa baki daya.

Alhassan Ado Doguwa yace Marigayiyar Mace ce Mai kyakykyawan Halaye Kuma uwa ce abar koyi saboda irin Tarbiyyar data baiwa ‘ya’yanta lokacin tana Raye.

“Salon yadda Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero da Dan uwansa Mai Martaba Sarkin Bichi Alhaji Nasiru Ado Bayero suke mulkar al’ummarsu ya nuna Hajiya Maryam Ado Bayero (Mai Babban Daki ) ta basu Tarbiyya ta Gari”. Inji Alhassan Ado Doguwa

Shugaban Masu Rinjayen yayi Mata addu’ar samun Rahamar Allah madaukakin Sarki tare d fatan Allah ya baiwa Iyalan da al’ummar jihar nan hakurin jire Wannan babban Rashin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...

Dubun wani magidanci da ke da’awar bin mamata bashi a Kano ta cika

Daga Aminu Gama   Kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a...

Abubuwan da aka tattauna tsakanin Peter Obi da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

Gwamna Bala Muhammed na jihar Bauchi ya ce a...