Iftila’i: Gobara ta kone kauyuka uku a jihar Jigawa

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Wata mummunar gobara da ta tashi a wasu ƙauyuka uku a cikin ƙaramar Kiyawa a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta janyo asarar dukiyoyi masu yawa.

 

 

Gobarar ta yi sanadin ƙonewar ɗaruruwan gidaje da amfanin gona da kuma dabbobi masu yawa.

 

 

Al’amarin ya auku ne ranar Lahadi da rana a ƙauyukan Malamawa da Karangiya da kuma Kwaleji.

 

Mutanen ƙauyukan sun kwana a bayan gari saboda gobarar ta ƙone musu gidajensu.

 

 

Rahotonni sun ce an kwashe lokaci mai tsawo kafin a iya kashe wutar sakamakon iskar da ke kaɗawa a kauyukan.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke wa wani hukuncin daurin gidan yari bisa laifin kona tayoyin mota a Kano

Ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi ta jihar Kano ta...

Bayan ficewa daga PDP Dino Melaye ya koma ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawan Najeriya mai wakiltar Kogi ta...

Ƴan Ghana na zanga-zangar neman korar ƴan Nijeriya daga ƙasar

  Zanga-zanga ta ɓarke a Ghana inda ake zargin ƴan...

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...