Iftila’i: Gobara ta kone kauyuka uku a jihar Jigawa

Date:

Daga Kamal Umar Kurna

 

Wata mummunar gobara da ta tashi a wasu ƙauyuka uku a cikin ƙaramar Kiyawa a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya ta janyo asarar dukiyoyi masu yawa.

 

 

Gobarar ta yi sanadin ƙonewar ɗaruruwan gidaje da amfanin gona da kuma dabbobi masu yawa.

 

 

Al’amarin ya auku ne ranar Lahadi da rana a ƙauyukan Malamawa da Karangiya da kuma Kwaleji.

 

Mutanen ƙauyukan sun kwana a bayan gari saboda gobarar ta ƙone musu gidajensu.

 

 

Rahotonni sun ce an kwashe lokaci mai tsawo kafin a iya kashe wutar sakamakon iskar da ke kaɗawa a kauyukan.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...