Sarki Salman na Saudiyya ya taya Tinubu murnar nasarar zaɓe

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Hadimin Masallatan Harami guda biyu, Sarki Salman na Saudiyya ya aike da sakon taya murna ga zababben shugaban ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu kan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasa.

 

A jawabin sa, Sarkin ya bayyana farin cikinsa ga zababben shugaban kasar bisa dukkan nasarorin da aka samu, inda ya yi fatan Allah ya kara wa gwamnati da al’ummar ƙasar albarka.

 

Shima a nasa jawabin, Yarima mai jiran gado kuma Firayim Minista Mohammed Bin Salman shi ma ya aike da sakon taya murna ga Tinubu kan nasarar da ya samu a zaben shugaban kasar Tarayyar Najeriya.

 

Yarima mai jiran gado, ya bayyana farin cikinsa ga zababben shugaban kasar bisa dukkan nasarorin da aka samu, inda ya yi fatan Allah albarka da ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...