Manufofi 6 da na ke son cimma idan na zama dan majalisar kura madobi da garun Mallam – Musa Iliyasu Kwankwaso

Date:

Daga Khadija Abdullahi Aliyu

 

Dan takarar majalisar wakilai na kura madobi da garun Mallam a tutar jam’iyyar APC Hon Dr Musa Iliyasu Kwankwaso ya fitar da wasu manufofin guda shida da yake son cimma idan al’ummar kananan hukumomin kura madobi da garun Mallam.

 

Hon. Musa Iliyasu Kwankwaso ya bayyana manufofin nasa ne yayin wata ganawa da yayi da Jaridar kadaura24.

 

Talla

Yace ya kamata duk wanda ya shirya Shugabanta ko wakiltar al’umma ya Samar da abubun da zai sanya a gaba idan Allah yasa ya zama abun da yake so ya zama, domin da haka ne zai iya magance matsalolin al’umma sa .

Talla daukar nauyi Hon. Surajo Umar Wudil

” Ni da yake nasan suwa zan wakilta hakan tasa na zauna na tsara abubuwan da zan Sanya a gaba idan na je majalisar wakilai ta kasa, ta yadda zan sami saukin sauke nauyin da al’ummar kananan hukumomin kura madobi da garun Mallam zasu dora min da yardar Allah”. Inji Musa Iliyasu

 

Yace zai Rika bin manufofin daya bayan daya har ya cimmu musu don inganta Rayuwar al’ummar kura madobi da garun Mallam cikin shekarun 4 farko da zai wakilci al’ummar sa a zauren majalisar wakilai ta kasa dake Abuja.

 

Ga manufofin da Hon. Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso ya ke son cimma idan ya zama dan majalisar tarayya.

 

1. Bunkasa aiyukan Noma

 

 

2. Bunkasa Ilimi a kananan hukumomin kura madobi da garun

 

3. Inganta harkokin kula da lafiyar al’umma.

 

4. Raya karkara

 

5 . Baiwa mata da matasa tallafin sana’o’in dogaro da kai

 

6. Wakilci na gari

 

 

Idan kuka cigaba da bibiyar mu zamu kawo muku bayani dalla-dalla akan wadancan manufofi na Dr. Musa Iliyasu Kwankwaso.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Sarkin Kano na 15 ya gana da Shugaba Tinubu kan rikicin Rimin Zakara

    Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado...

Da dumi-dumi: Tinubu ya baiwa sakataren jam’iyyar APC na Kano mukami

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Sakataren jam’iyyar APC na jihar Kano,...

Gwamnatin Kano ta haramtawa yan kwangila zuwa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar – Kwamishina

Gwamnatin kano ta ja kunnen yan kwangilar ayyukan kananan...

Iftila’i: Almajirai 17 sun kone kurmus 15, sun jikkata sanadiyya wata gobara

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Wata gobara da ta tashi ta...