Ba za mu kara wa’adin Chanjin kuɗi daga 10 ga Fabrairu ba, Emefiele ya gargadi ‘yan Najeriya

Date:

Daga Abdulrashid B Imam

 

 

Babban bankin Najeriya (CBN) ya ce ba ya tunanin kara tsawaita wa’adin karɓar tsoffin kudaden da aka sauya musu fasali ba.

 

 

‘Yan Najeriya ciki har da gwamnonin da aka zaba a karkashin jam’iyyar APC, sun bukaci babban bankin kasar da ya kara tsawaita wa’adin, sakamakon karancin kudin da aka yi wa kwaskwarima a cikin al’umma.

Talla

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

Sai dai gwamnan babban bankin na CBN, Godwin Emefiele, ya ce bankin ba ya tunanin tsawaita wa’adin bayan wa’adin kwanaki 10 da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da shi kwanan nan.

 

 

Emefiele, wanda ya bayyana hakan a wani taron karawa juna sani da aka yi a Legas, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su yi hakuri ganin cewa nasarorin da aka samu a manufofin sun fi kalubalen yawa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...

Iftila’i: An Sami Ambaliyar Ruwa a garin Maiguduri

Mazauna wasu yankuna a Maiduguri, babban birnin jihar Borno...

Shugabanni ku rika gudanar da aiyukan da za su rage talauci a cikin al’umma – SKY

Daga Kamal Yakubu Ali   Fitaccen dan kasuwa a Kano Alhaji...

Muna da yakinin APC za ta lashe zabuka a Kano da Arewa don Tinubu ya yi tazarci a 2027 – Alfindiki

Jigo a jam’iyyar APCn Kano, Comrade Faizu Alfindiki, ya...