Ku magance matsalar ƙarancin kuɗi da yan ƙasar suke fuskanta – Atiku ya fadawa CBN

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

 

Ɗan takarar shugabancin Najeriya ƙarƙashin jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya yi kira ga Babban Bankin ƙasar CBN da ya magance wahalhalun da ‘yan ƙasar ke fuskanta na ƙarancin sabbin takardun kuɗi a faɗin ƙasar.

 

A wata sanarwa da ofishin yaƙin neman zaɓensa ya fitar, Atiku ya yi kira ga Babban Bankin da ya gaggauta sake duba matakan da ya ɗauka, domin ya wadata al’umma da sabbin takardun kuɗin.

 

Yayin da yake yaba wa Babban Bankin kan sauraron koken talakawan ƙasar, tare da yin ƙarin wa’adin kwana 10 na amfani da tsoffin takardun kudin ƙasar, Atiku ya yi kira ga Babban Bankin da ya sake duba matakan da ya ɗauka domin tabbatar da cewa an samu wadatattun sabbin takardun kuɗin a cikin al’umma.

Talla

 

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kotu ta yanke wa wani hukuncin daurin gidan yari bisa laifin kona tayoyin mota a Kano

Ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi ta jihar Kano ta...

Bayan ficewa daga PDP Dino Melaye ya koma ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawan Najeriya mai wakiltar Kogi ta...

Ƴan Ghana na zanga-zangar neman korar ƴan Nijeriya daga ƙasar

  Zanga-zanga ta ɓarke a Ghana inda ake zargin ƴan...

Rikicin gida: Jam’iyyar APC ta Fara Tuhumar Kakakinta na Kano Ahmad S Aruwa

Daga Abdullahi Shu'aibu Hayewa   Jam'iyyar APC ta Mazabar Daurawa a...