Daga Kamal Umar Kurna
Wata babbar kotun tarayya da ke Kano ta bayar da umarnin kamawa, bincike da kuma gurfanar da shugaban jam’iyyar APC, Abdullahi Abbas.
A karar da Mahmoud Lamido ya shigar, ana zargin shugaban jam’iyyar da yin kalaman tunzura al’umma, da kawo cikas ga zaman lafiya, da kuma kalaman da basu dace.
Lawan Lamido Bashir Yusuf Muhammad, ya shaida wa kotun cewa Abdullahi Abbas ya yi barazanar kashe wanda yake karewa ta wayar tarho.

Alkalin kotun, Mai shari’a S. A. Amobeda, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 16 ga watan Fabrairu 2023.

Jam’iyyar NNPP ta yi murna da wannan cigaba kasancewar hakan zai kara kare damakaradiyya, saboda wanda ake karar ta jima yana kalaman tunzura al’umma.
Babban Mai magana da yawun kwamitin yakin neman zaben jam’iyyar NNPP a kano Sanusi Bature Dawakin Tofa yace a kwanakin baya wata kotu daban ta baiwa kwamishinan ‘yan sandan jihar kano umarnin kama Abdullahi Abbas saboda irin kalaman tunzura al’umma da yake yi