Karancin Man Fetur ka iya shafar zabe a Nigeria – INEC

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC ta ce matsalar ƙaramncin man fetur da ƙasar ke fuskanta ka iya shafar tsare-tsaren hukumar game da za ta shirya zaɓen ƙasar da ke tafe.

Shugaban Hukumar Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka ranar Talata a Abuja a lokacin taron tuntuɓa tsakanin hukumar da ƙungiyoyin direbobin haya na ƙasar waɗanda suka haɗar da NARTO da NURTW da sauransu.

“Hukumar zaɓe tana tare da ku game da kokenku na ƙarancin man fetur da ƙasar nan ke fuskanta, da yadda hakan zai shafi hakar sufuri musamman a ranar zaɓe,” in ji Mahmood.

Ya ƙara da cewa “magana ta gaskiya ita ce rashin wadataccen man zai shafi shirye-shiryenmu”. Inji Farfesa Mahmoud

Talla

Shugaban hukumar ya ce dangane da wannan dalili , hukumar zaɓe za ta gana da kamfanin mai na ƙasa NNPCL domin duba hanyoyin da ya kamata a bi wajen magance wannan matsala.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Muna bukatar kayan aiki domin magance matsalar tsaro a karamar hukumar Nasarawa – Muhd Haruna Black

Kwamandan Jami'an sintiri na karamar hukumar Nasarawa a jihar...

Da dumi-dumi: An Sanya dokar Hana fita a Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta sanya dokar taƙaita zirga-zirga ta tsawon...

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...