Ba mu Kara Kudin Man Fetur a Nigeria ba – NNPC

Date:

Shugaban kamfanin mai na NNPCL Malam Mele Kyari ya ce babu wanda ya kara farashin mai a Najeriya.

Shugaban ya musanta iƙirarin da wasu kungiyoyin masu dakon mai suka yi a baya na cewa an ƙara farashi.

Mele ya bayyana hakan ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudana a yau Talata kan matsalar karancin mai da ake fama da ita a Najeriya.

Cikin matsalolin da aka ambato da ake ganin su suke kawo tarnaƙi ga man sun haɗa da bangare jigilar man da kuma bangare farashin da aka gaza samun daidaito.

Mele ya kalubalanci duka masu ruwa da tsakin da suka halarci taron da su bayyana wanda ya ce musu an kara farashin man, ko kuma su gabatar da hujjar sun saye shi a sabon farashin da suka yi ikirari.

Talla

Tun a baya dai shugaban masu gidajen mai masu zaman kansu reshen ihar Kano Bashir Danmallam ya tabbatar wa BBC Gwamnatin Najeriya ta ƙara farashin man fetur a hukumance da kashi 8.8 inda a halin yanzu farashin ya koma naira 185 Legas da kuma 220 a wasu sassa.

Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil

A Najeriya dai an shafe kusan shekar a guda ana karancin man fetur da kuma rashin tabbas kan farashinsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Yanzu-Yanzu: An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata saboda wasu dalilai

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika sakon ta’aziyyar Rasuwar Aminu Dantata

Daga Sadiya Ahmad   Kungiyar Farfado da martabar Arewa ta Mika...

Kungiyar ’Yan Jaridun Kano Arewa ta Aike da Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Alhaji Aminu Dantata

  Kungiyar ’Yan Jarida ta Kano Arewa ta bayyana alhinin...

Ku na da rawar takawa wajen inganta Lafiyar al’ummar Kano – Waiya ga jami’an yada labarai

Daga Abubakar Sayeed Kwamishinan Ma'aikatar yada labarai da harkokin cikin...