Kungiyoyin makarantun Islamiyya na Ƙaramar Hukumar Nassarawa da ƙungiyar tallafa wa matasa ta Kudancin Nassarawa, da ke Unguwar Badawa, sun gudanar da taron Maulidi, inda suka nada Sakataren Jam’iyyar APC na Mazabar Giginyu, Hon. Isah Ado Muhammad Badawa, a matsayin Majidadin Tallafawa Makarantun Islamiyya.
Babban malamin Unguwar Badawa, Malam Gwani Kanzu Badawa, tare da takwaransa Malam Saminu Gidan Salati, sun bayyana cewa an bai wa Hon. Isah Ado Muhammad Badawa wannan sarauta ne bisa la’akari da irin gudunmawar da yake bayarwa wajen tallafa wa harkokin addinin Musulunci, da kuma taimaka wa matasa da marayu a yankunan Ƙaramar Hukumar Nassarawa.

Da yake jawabi, Injiniya Usman Taye Ahmed, Daraktan Sashen Ayyuka na Ƙaramar Hukumar Nassarawa, ya bayyana farin cikinsa kan karrama Hon. Isah Ado Muhammad Badawa da wannan sarauta, yana mai cewa an sanya wa kowa abin da ya dace da shi.
Shi ma a nasa jawabin, Sakataren Jam’iyyar APC na Mazabar Giginyu kuma sabon Majidadin Tallafawa Makarantun Islamiyya da Matasa, Hon. Isah Ado Muhammad Badawa, ya gode wa ƙungiyoyin da suka ga cancantarsa tare da ba shi wannan matsayi.
Isah Ado Muhammad Badawa ya ce bai san cewa al’ummar yankunan Ƙaramar Hukumar Nassarawa na lura da irin gudunmawar da yake bayarwa ba, har sai da suka yanke shawarar karrama shi da wannan sarauta.

Ya kuma gode wa waɗanda suka karrama shi bisa la’akari da irin gudunmawar da yake bayarwa wajen tallafa wa makarantun Islamiyya, matasa da kuma harkokin siyasa.
A ƙarshe, ya yi kira ga al’ummar yankunan da su ci gaba da ba Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, goyon baya, tare da ba shi damar sake jagorantar jihar a wa’adi na biyu.