Sanata Barau Na Ci Gaba Da Raba Takin Noma Na Zamani Kyauta A Kabo, Bagwai Da Dawakin Tofa

Date:

A yau ne aka ci gaba da rabon Takin Noma na Zamani kyauta ga manoma a ƙananan hukumomin Kabo, Bagwai da Dawakin Tofa, a matsayin wani ɓangare na shirin tallafa wa harkokin noma da inganta samar da abinci.

Shirin, wanda Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, CFR, ya ɗauki nauyi, na ci gaba da kawo sauƙi ga dubban manoma a yankin Kano ta Arewa ta hanyar samar musu da takin noma ba tare da sun biya komai ba.

IMG 20251224 WA0004

Manoman da suka amfana sun bayyana farin cikinsu kan wannan tallafi, suna mai cewa zai taimaka musu wajen ƙara yawan amfanin gona tare da rage musu nauyin kashe kuɗaɗen noma.

Wannan shiri na daga cikin ƙoƙarin Sanata Barau na ƙarfafa fannin noma, inganta rayuwar al’umma, da kuma tallafawa manufofin samar da wadataccen abinci a ƙasa.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnan Kano ya raba kyautar filaye da kudade ga masu rike da mukami a gwamnatin sa

Gwamnan Jihar Kano, Abba Yusuf, ya bayyana cewa gwamnatinsa...

Sabon Rikici ya Ɓarke Tsakanin Ma’aikata da Hukumar Kamfanin BAGCO A Kano

Wani sabon rikici ya ɓarke tsakanin ma’aikatan Kamfanin BAGCO...

Abba Ya Sauya Fasalin Kano” – Ɗan Majalisar Takai/Sumaila Ya Yabawa Gwamnan Kano

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Kananan hukumomin Sumaila/Takai, Barrista...

Kwamitin Tsaro na Dorayi Ya Koka Kan Rashin Tallafi, Ya Yi Barazanar Dakatar da Ayyukansa

Daga Aliyu Danbala Gwarzo Kwamitin Tsaro na Unguwar Dorayi a...