Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Date:

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai na farko tun kafuwarta, inda ta yaye ɗalibai 177 daga sassan kimiyya da ilimin zamantakewa.

Shugaban jami’ar, Farfesa Adamu Idris Tanko, ya bayyana cewa ɗalibai 22 sun samu First Class wato daraja ta daya da ɗalibai 57 suka samu daraja ta biyu wato Second Class Upper da 65 suka samu Second Class Lower sai ɗalibai 32 suka samu Third Class, yayin da ɗaya ya samu makin tsallakewa.

Fitattun dalibai biyu mata, Amina Anna Kabir da Nwachukwu Esther Kelechi, sun samu CGPA na 4.97 daga 5.00, kuma mata ne 19 daga cikin waɗanda suka samu First Class.

InShot 20250309 102512486

Farfesa Tanko ya ce wasu daga cikinsu za a ɗauke su aiki a matsayin kananan Malamai.

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

Haka kuma, jami’ar ta bai wa fitaccen malamin Alƙur’ani, Ustaz Ahmad Sulaiman Ibrahim, digirin girmamawa na Doctor of Letters (Honoris Causa) saboda gudummawar sa ga ilimin addini.

Bikin ya samu halartar manyan jami’an gwamnati da malamai da ‘yan kasuwa, inda aka yaba da ci gaban jami’ar wajen samar da ɗalibai masu nagarta da ƙwarewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar Sojin Amuruka ta kammala tsara yadda za ta kawo wa Nigeria hari

  Rundunar sojin Amurka da ke Afirka, AFRICOM, ta gabatar...

Kalaman Trump: Gwamnatin Nigeria ta Fara tattaunawa da Gwamnatin Amuruka

Gwamnatin Najeriya ta ce a gwamnantance tana tattaunawa da...

Ba zan bar Siyasa ba har lokacin da zan bar Duniya – Mal Shekarau

Tsohon Gwamnan jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau ya ce...

Barazanar Amuruka: Tinubu ya bukaci yan Nigeria su kwantar da hankulansu

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga...