Da dumi-dumi: ASUU ta dakatar da yajin aikin da ta fara

Date:

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) ta dakatar da yajin aikin gargadi na makonni biyu da ta fara a makon da ya gabata a dukkan jami’o’in gwamnati a faɗin ƙasar.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Chris Piwuna, ne ya sanar da hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a babban ofishin ASUU da ke Abuja a ranar Laraba.

Farfesa Piwuna ya bayyana cewa an yanke wannan shawara ne bayan shiga tsakani daga Majalisar Dattawa tare da wasu masu ruwa da tsaki, domin samar da fahimtar juna tsakanin gwamnati da ƙungiyar.

Sai dai ya ƙara da cewa, Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) ta ASUU ta ba wa gwamnatin wa’adin wata guda domin magance matsalolin da suka haddasa yajin aikin, inda ya yi gargadin cewa ƙungiyar za ta ɗauki mataki mafi tsanani idan aka kasa cika alkawura.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Pyramid of Heart sun kai tallafin na’urar Oxygen Concentrated Asibitin Murtala dake Kano

Asibitin Ƙwararru na Murtala Muhd dake Kano ya yabawa...

Ba mu da wata matsala da Ofishin mataimakin shugaban Kasa – NAHCON

Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta karyata wani rahoto...

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nemi hukumar NBC ta fadada aikinta kan kafafen yada labarai na intanet

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bukaci Hukumar...

RMK@69: Kwankwaso Jagora Ne Mai Hangen Nesa, Abba Kuma Na Kawo Ci Gaba a Kano – Bakwana

Wani jigo a kungiyar Kwankwasiyya, kuma tsohon mai ba...