Gwamnatin Kano ta sake maka Ganduje da ya’yansa a gaban Kotu

Date:

Gwamnatin jihar Kano ta kai tsohon gwamnan jihar, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, da ‘ya’yansa biyu da wasu mutum shida kotu bisa zargin yin almundahanar kudi naira biliyan 4.49.

Gidan talabijin na Channels ya rawaito cewa an shigar da karar ne a babbar kotun jihar Kano a ranar 13 ga Oktoba, 2025, inda gwamnati ke neman a maido da kashi 20 cikin 100 na kudaden da aka zuba a Dala Inland Dry Port Limited, da kuma dawo da kudin da ake zargin an karkatar.

InShot 20250309 102512486
Talla

Wadanda ake tuhuma sun hada da Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ‘ya’yansa Umar da Muhammad, tsohon mai ba shi shawara Abubakar Sahabo Bawuro, tsohon sakataren hukumar Nigerian Shippers Council Hassan Bello, lauya Adamu Aliyu Sanda, da kamfanin Dala Inland Dry Port Limited.

A cewar takardar tuhumar, ana zargin wadanda ake tuhumar da laifuka goma da suka hada da hada baki wajen karkatar da kudaden al’umma, cin amana da kuma sabawa doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta koka da kalaman mataimakin gwamnan Kano

Kungiyar Ma’aikatan Jinya da Ungozoma ta Najeriya (NANNM) reshen...

Kotu a Kano ta hukunta masu shago saboda zubar da shara a kan titi

Kotun tafi da gidanka da ke Kano ta yanke...

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama mata da maza da ke aikata badala

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama mata hudu...

Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Magantu Kan Batun Sheikh Abduljabbar

Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano ta bayyana cewa...