Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya Zama sabon shugaban gidan Radiyon Guarantee

Date:

Gidan Radiyo Guarantee Radio dake Kano ya sanar da nadin Abubakar Balarabe Kofar Naisa a matsayin Babban Manajan tashar, wanda zai fara aiki daga ranar 8 ga Oktoba, 2025.

Abubakar Balarabe Kofar Naisa kwararren dan jarida ne da dade yana ba da gudunmawa a fannin yada labarai, shugabancin kafafen watsa labarai.

Nadinsa ya nuna kokarin tashar na ƙarfafa jagorancinta da kuma ci gaba da jajircewar ta wajen samar da shirye-shiryen da ke ilmantarwa, nishadantarwa da kuma faɗakar da al’umma a fadin Jihar Kano.

Yayin da ya karɓi aiki a yau, Kofar Naisa ya nuna godiya bisa amincewar da aka yi da shi har aka ba sashi jagorancin tashar, sannan ya yi alkawarin yin aiki tukuru tare da sauran ma’aikata da shugabannin tashar don ci gaba da tabbatar da hangen nesa na guarantee radio wajen aiki da ƙwarewa don hidimtawa al’umma.

Ya ce a karkashin jagorancinsa Guarantee Radio 94.7 FM zai ta tabbatar da ta ci gaba da bin ƙa’idodin aikin jarida don cigaban al’umma masu sauraron tashar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Majalisu na neman sauya lokacin zabuka a Nigeria

Majalisar Dokoki Ta Ƙasa Ta Gabatar Da Kudirin Sauya...

Kungiyar Lauyoyi yan asalin jihar Kano sun mika korafi ga kasashen Amuruka Ingila da UN kan zargin kisan a Tudun Wada

Kungiyar Lauyoyin Yan Asalin Jihar Kano (National Forum of...

Da dumi-dumi: ASUU ta sanar da ranar da zata fara yajin aiki

Shugabancin Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta umurci...

Kananan Hukumomin Tarauni Rogo da Doguwa sun zamo koma baya wajen yin rijistar Masu zabe a Kano

Rahotanni sun nuna cewa ya zuwa yanzu kananan hukumomin...