‎Sarki Sanusi II ya bayyana hanyoyi 7 da za a magance talauci a Nigeria

Date:


‎Najeriya ta daɗe tana fuskantar matsalolin talauci da hauhawar farashin kaya, da rashin tabbas a harkokin tattalin arziki, kodayake a baya-bayan nan an ɗan amu sauƙi.

‎Duk da kasancewarta ƙasa mai dimbin arziki, akwai miliyoyin ‘yan ƙasar da ke rayuwa a cikin tsananin talauci, inda rashin aikin yi da rashin wadatacciyar wutar lantarki da hauhawar farashin kayayyaki ke ƙara dagula rayuwar al’umma.


‎A wani taron neman mafitar makomar tattalin arziƙin Najeriya zuwa shekarar 2030, wanda ‘News Central’ ta shirya, Sarkin Kano na 16 kuma tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana wasu shawarwari kan yadda za a iya rage talauci a ƙasar.

‎Sarki Sanusi ya jaddada cewa babban mataki shi ne tabbatar da daidaito a ɓangaren tattalin arziki saboda cimma duk wata manufa ta ci gaban ƙasa.

‎Sarkin ya bayar da shawarwari kan hanyoyin da za a bi domin kaucewa talauci a ƙasar kuma sun haɗa da:

‎1. Samar da Ilimin yaya mata

‎2. Daidaiton tattalin arzikin Kasa

‎3. Kayyade farashin Dala


‎4. Tabbatar da ingantaccen tsarin Ilimi

‎5. Samar da wadatacciyar wutar Lantarki

‎6. Jajircewa da Hakuri don samun cigaba

‎7. Inganta hanyoyin kashe kudaden wajen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...