Yadda Dansanda ya harbe kansa da bindiga a Kano

Date:

Wani jami’in dansanda mai suna Aminu Ibrahim ya rasa ransa sakamakon harbin kansa da bindiga da yayi bisa kuskure lokacin da yake bakin aiki a jihar Kano.

A cewar daily trsut, lamarin ya faru ne da misalin karfe 5:40 na safiyar ranar Asabar a unguwar Hotoro.

Rahotanni sun ce jami’in da ke aiki a rundunar ƴansandan jihar Kano, ya shiga bandaki a harabar Kamfanin Basnaj Global Resources Limited, lokacin da bindigarsa ta harba.

Binciken farko ya nuna cewa Ibrahim ya harbe kansa a ciki yayin da yake tsugunawa da bindigarsa kirar AK-47 da ke rataye a wuyansa.

Bindigar mai lambar rajista GT 4177, an same ta tare da harsashi guda daya da ya harba, yayin da aka lissafa harsasai 29 daga cikin 30 da aka ba shi a farko.

An garzaya da shi asibiti inda aka tabbatar da rasuwarsa, sannan aka kai gawarsa dakin ajiye gawa domin yi masa gwajin gano musabbabin mutuwarsa.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana cewa har yanzu ana bincike kan lamarin, kuma za su bayyana sakamakon nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince...

Kudade: Ganduje ya caccaki Gwamnatin kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Tsohon shugaban jam’iyyar APC...

Gwamnan Kano ya tura sunayen mutane biyu majalisar dokokin don nada su a mukaman Kwamishinoni

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mika...

NLC Reshen Kebbi Ta Soki Cire Naira Miliyan 14 Daga Albashin Malamai

Kungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC) reshen Jihar Kebbi, ta...