Al’ummar Tokarawa, Gorubai, Garawa da Yarawa sun koka kan matsalar hanya da rashin gada

Date:

Al’ummar garuruwan Tokarawa, Gorubai, Garawa, Yarawa da Dan Tsuku da ke cikin karamar hukumar Nasarawa a Kano sun koka kan matsalar rashin hanya da kuma rashin gada da za ta taimaka musu wajen ketare wani rafin da ya kasance babban kalubale ga rayuwarsu.

Mazauna yankin sun bayyana wa wakilinmu cewa tsawon shekaru suna fama da matsalolin zaizayar ƙasa da kuma rashin wadatattun hanyoyin da za su sauƙaƙa musu rayuwa, musamman a lokacin damina.

Daya daga cikin dattawan yankin, Malam Sani Haruna Baba, ya ce sun shafe shekaru suna fuskantar matsalar rashin gada da za ta haɗa su da sauran unguwanni.

“Unguwanninmu babu hanya, babu asibiti, babu hasken wutar lantarki. Mata masu juna biyu kan rasa rayukansu idan aka daukos su zuwa Asibitin Sir Sunusi ko Murtala. ’Yan siyasa kuma sun manta damu a karamar hukumar Nasarawa,” in ji Malam Baba.

Shi ma wani mazaunin yankin, Malam Muhammadu Lawan Garawa, ya bayyana cewa matsalar rashin gada ta haddasa cikas har a al’amuran aure.
Ya ce:

> “Saboda wannan matsalar, mutane basa son zuwa neman aure a garuruwanmu, ga kuma matsalar rashin makarantun da suka dace.”

Shugaban ƙungiyar cigaban al’ummar yankin (INA MAFITA), Shu’aibu Ibrahim Aramma, ya bukaci gwamnatin Kano ƙarƙashin Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf, da sauran wakilai a matakin jiha da tarayya da su kawo musu agajin gina gada domin rage musu wahala.

“Mai Girma Gwamna, muna roƙon Allah ka zo ka gani da idonka. Muna cikin ƙunci sosai, har akwatin zabe babu a yankinmu, kamar ba Kano muke ba,” in ji Shu’aibu.

Wakilinmu ya nemi jin ta bakin shugaban karamar hukumar Nasarawa kan wannan batu, amma ya rawaito cewa shugaban ya bukaci al’ummar yankin su kai korafinsu a rubuce.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kungiyar ODPMNigeria ta shirya taron tattaunawa da matasa a Bichi

Daga Ahmad Isa Getso   Ƙungiyar Rajin Kawo Sauyi da Cigaba...

Yadda Dansanda ya harbe kansa da bindiga a Kano

Wani jami’in dansanda mai suna Aminu Ibrahim ya rasa...

Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince...

Kudade: Ganduje ya caccaki Gwamnatin kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Tsohon shugaban jam’iyyar APC...