Kwankwaso ya Magantu kan Batun Rubuta Takardar Neman Shiga APC

Date:

Tsahon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya musanta labarin da ake yadawa cewa ya rubutawa jam’iyyar APC bukatar shiga cikin Jam’iyyar.

A jiya alhamis ne dai aka ta yada labarin wanda har aka ce shi ne dalilin da yasa masu ruwa da tsakin jam’iyyar APC na jihar Kano sun gudanar da wani taron gaggawa a Abuja .

A wata sanarwa da Kwankwaso ya fitar da Safiyar Wannan rana ta juma’a ya ce labarai ba shi da tushe ballantana makama

Yace “An wayi gari da jita-jitar da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa mun gabatar da takardar nuna sha’awar shiga wata jam’iyyar siyasa a kasar nan.

Kwankwaso ya fito fili ya nesanta kansa daga wannan batu, inda ya bayyana cewa ba su taba mika irin wannan takarda ga kowacce jam’iyya ba.

A cikin sanarwar Jagoran jam’iyyar NNPP na Kasa ya ce yana shawartar jama’a da su ci gaba da bibiyar sahihan hanyoyin da aka tanada na ofishinsa domin samun ingantattun bayanai game da lamuransa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar jin daɗin alhazai ta Kano ta sanar da kuɗin aikin hajjin badi

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta amince...

Kudade: Ganduje ya caccaki Gwamnatin kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma Tsohon shugaban jam’iyyar APC...

Gwamnan Kano ya tura sunayen mutane biyu majalisar dokokin don nada su a mukaman Kwamishinoni

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya mika...

NLC Reshen Kebbi Ta Soki Cire Naira Miliyan 14 Daga Albashin Malamai

Kungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC) reshen Jihar Kebbi, ta...