Kwankwaso ya Magantu kan Batun Rubuta Takardar Neman Shiga APC

Date:

Tsahon gwamnan Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya musanta labarin da ake yadawa cewa ya rubutawa jam’iyyar APC bukatar shiga cikin Jam’iyyar.

A jiya alhamis ne dai aka ta yada labarin wanda har aka ce shi ne dalilin da yasa masu ruwa da tsakin jam’iyyar APC na jihar Kano sun gudanar da wani taron gaggawa a Abuja .

A wata sanarwa da Kwankwaso ya fitar da Safiyar Wannan rana ta juma’a ya ce labarai ba shi da tushe ballantana makama

Yace “An wayi gari da jita-jitar da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewa mun gabatar da takardar nuna sha’awar shiga wata jam’iyyar siyasa a kasar nan.

Kwankwaso ya fito fili ya nesanta kansa daga wannan batu, inda ya bayyana cewa ba su taba mika irin wannan takarda ga kowacce jam’iyya ba.

A cikin sanarwar Jagoran jam’iyyar NNPP na Kasa ya ce yana shawartar jama’a da su ci gaba da bibiyar sahihan hanyoyin da aka tanada na ofishinsa domin samun ingantattun bayanai game da lamuransa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...