Gwamnan Bauchi ya nada ɗan ƙasar China a matsayin mai bashi shawara kan tattalin arziƙi

Date:

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya nada Mista Li Zhensheng, ɗan ƙasar China, a matsayin mai ba da shawara kan tattalin arziƙin jihar.

FB IMG 1753738820016
Talla

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa an sanar da hakan ne yayin rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar da cibiyar China Global Promotion Cooperation Research Centre.

Gwamnati da Malamai a Kano sun fitar da mafi karanci kudin sadaki da Zakka da Diyar Rai

Yarjejeniyar na nufin haɓaka zuba jari, bunƙasa gine-gine, da haɗin kai a fannoni kamar noma, ilimi, kiwon lafiya, masana’antu, hakar ma’adinai, da kasuwanci.

Za a kuma buɗe ofishin wakilan Bauchi a ƙasar China domin sa ido kan aiwatar da ayyuka.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Gwamna Bala ya ce haɗin gwiwar ta dace da manufofin diflomasiyya tsakanin shugabannin ƙasashen Najeriya da China, kuma za ta taimaka wajen samar da ayyukan yi, haɓaka ƙwarewa, da ƙara wa Bauchi suna a duniya.

Mista Zhensheng ya yi alƙawarin kawo goyon bayan cibiyarsa domin ci gaba mai ɗorewa a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...

A Hukuma ce INEC ta bayyana sakamakon zabukan cike gurbi da aka yi a kano

Hukumar zabe mai zamanta ta Kasa ta bayyana Dan...

PDP ta yi watsi da zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono dake Kano

Jam’iyyar PDP reshen jihar Kano Arewa maso Yammacin Najeriya...

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...