Gwamnan Bauchi ya nada ɗan ƙasar China a matsayin mai bashi shawara kan tattalin arziƙi

Date:

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya nada Mista Li Zhensheng, ɗan ƙasar China, a matsayin mai ba da shawara kan tattalin arziƙin jihar.

FB IMG 1753738820016
Talla

Jaridar PUNCH ta rawaito cewa an sanar da hakan ne yayin rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin gwamnatin jihar da cibiyar China Global Promotion Cooperation Research Centre.

Gwamnati da Malamai a Kano sun fitar da mafi karanci kudin sadaki da Zakka da Diyar Rai

Yarjejeniyar na nufin haɓaka zuba jari, bunƙasa gine-gine, da haɗin kai a fannoni kamar noma, ilimi, kiwon lafiya, masana’antu, hakar ma’adinai, da kasuwanci.

Za a kuma buɗe ofishin wakilan Bauchi a ƙasar China domin sa ido kan aiwatar da ayyuka.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

Gwamna Bala ya ce haɗin gwiwar ta dace da manufofin diflomasiyya tsakanin shugabannin ƙasashen Najeriya da China, kuma za ta taimaka wajen samar da ayyukan yi, haɓaka ƙwarewa, da ƙara wa Bauchi suna a duniya.

Mista Zhensheng ya yi alƙawarin kawo goyon bayan cibiyarsa domin ci gaba mai ɗorewa a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...