Gwamnan Kano ya baiwa jami’an tsaro umarnin Kamo yan daban da suka yi sanadiyyar rasuwar hadiminsa

Date:

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya baiwa jami’an tsaro umarnin Kamo duk wanda yake da hannu a sanadiyyar mutuwar hadiminsa Sadiq Gentle.

“Ina matukar alhinin game da rasuwar Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman a ma’aikatar tarihi da al’adu ta jihar Kano, wanda ya rasu sakamakon raunukan da ya samu a wani mummunan harin da wasu da ake kyautata zaton ‘yan daba ne suka kai a baya-bayan nan”.

FB IMG 1753738820016
Talla

A cikin sakon ta’aziyyar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa kadaura24, gwamna Yusuf ya bayyana marigayi Gentle a matsayin “kwararre mai kishin al’umma a kafafen sada zumunta” wanda mutuwarsa ta tashin hankalin gwamnatin jihar da kuma kafafen sada zumunta.

2027: Jonathan zai tsaya takarar shugaban ƙasa don karawa da Tinubu
.
“Na yi matukar bakin ciki lokacin da na Sami labarin rasuwar Malam Sadiq Gentle,” in ji Gwamnan.

Gwamna Yusuf ya yi Allah-wadai da kisan da kakkausar murya, yana mai bayyana shi a matsayin “mummunan abun da ba za a amince da shi ba.”

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

.
Gwamnan ya kuma mika sakon ta’aziyya ga iyalan Gentle da abokan arziki da kuma abokan aikinsu, yana mai tabbatar musu da cewa gwamnatin jihar Kano za ta kasance da su a wannan mawuyacin yanayi.
.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilan da suka sa Kwankwaso ba zai hada hanya da Tinubu a zaben 2027 ba – Buba Galadima

Guda cikin jiga-jigan jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce...

Adam A Zango ya sake Aurar Jarumar Kannywood

Fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finan Hausa, Kannywood, Adam A....

NNPP ta yi watsi da sakamakon Zaben Ghari da Tsanyawa a Kano

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta ƙi amincewa da...

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...