Mafi yawan yan Siyasar Nigeria ba su da tarbiya – Sarki Sanusi II

Date:

Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi II ya zargi ‘yansiyasar Najeriya da aikata cin hanci da rashawa saboda “rashin tarbiyya tun daga tasowarsu”.

Da aka tambayi sarkin ta cikin shirin Politics Today na kafar talabijin ta Channels TV a yammacin yau dangane da cin hanci da rashawa, Sanusi ya ce da yawa ba a koya musu yin gaskiya da riƙon amana ba.

FB IMG 1753738820016
Talla

“Akasarin mutanen da ke riƙe da ofisoshin gwamnati ba su da wannan tarbiyyar, mafi yawa na shiga gwamnati ne bisa dalilai marasa kyau,” in ji shi.

Kanana da matsakaitan yan kasuwar Abubakar Rimi ta Sabon gari sun bukaci Gwamnan Kano ya shiga cikin lamarinsu

“Ina ganin an rusa kusan baki ɗayan ɗabi’un kirki na ƙasar nan. Marasa tarbiyya ne suke mulkar mu, waɗanda ba su da wani abin alfahari kuma ba su da niyyar barin wani abin alfahari a bayansu.

“Mutane ne da ke alfahari kawai da yawan dukiyarsu, da yawan gidaje, da yawan jiragen da suka mallaka. Ba su taɓa tunanin cewa mutane na yi musu kallon ɓarayi ne.

IMG 20250802 WA0088(1)
Talla

“Ba matsalar mutum ɗaya ba ce, shugaban ƙasa ko gwamna. Ku duba yadda shugabannin addininmu suka zama ‘yan bambaɗanci, su ma sarakuna suka kiɗime. Kusan kowa ya auka cikin wannan ruɗanin.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dalilan da suka sa Kwankwaso ba zai hada hanya da Tinubu a zaben 2027 ba – Buba Galadima

Guda cikin jiga-jigan jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce...

Adam A Zango ya sake Aurar Jarumar Kannywood

Fitaccen jarumin masana’antar shirya fina-finan Hausa, Kannywood, Adam A....

NNPP ta yi watsi da sakamakon Zaben Ghari da Tsanyawa a Kano

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta ƙi amincewa da...

Kwankwaso ya yi tsokaci game da zaben cike gurbi da akai a Kano

Jagoran jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana...