Za’a dade ana tunawa da irin gudunmawar da Alhaji Aminu Dantata ya bayar a duniya – Sarki Aminu Bayero

Date:

Daga Abdulmajid Habib Tukuntawa

 

Bayan dawowarsa daga garin Madina dake Kasar Saudia Arabia domin jagorantar jana’izar Marigayi Alhaji Aminu Dantata Mai Martaba Sarkin Kano na 15 Alhaji Aminu Ado Bayero ya ziyarci iyalan Marigayi Alhaji Aminu Dantata domin yi musu Ta’aziyyar rasuwarsa.

Alhaji Aminu Ado Bayero ya ce duniya baki daya ba zata manta da irin gudunmawar da Alhaji Aminu Alhasan Dantata ya bayar ba wajen cigaba a fannoni daban daban.

InShot 20250309 102512486
Talla

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban sakataren Sarkin Abubakar Balarabe Kofar Na’isa ya aikowa Kadaura24.

Mai Martaba Sarkin ya jagoranci gabatar da addu’o’i na musamman ga marigayin inda yayi addu’ar Allah ya jaddada rahama ga Marigayin ya Kuma bawa iyalansa da al’umar jihar Kano da Kasa da duniya baki daya hakurin jure rashinsa.

Da dumi-dumi: Sanarwa ta Musamman daga Alhaji Kabiru Sani Kwangila Yakasai SKY

Kazalika Mai Martaba Sarkin yakan makamanciyar irin wannan ziyarar Ta’aziyyar ga Hajiya Mariya Dantata inda yayi addu’ar Allah ya gafarta masa ba bashi aljanna madaukakiya.

Kamar kowanne lokaci dai Mai Martaba Sarkin ya samu rakiyar Hakimai da sauran al’umma masoya Sarki tun daga fitowarsa zuwa komawa fadarsa dake gidan Nassarawa a birnin Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rikicin Sarautar Kano: Fadar Sarki Sanusi ta zargi magoya bayan Sarki Aminu Ado Bayero da kai farmaki Kofar Kudu

Daga Sani Idris Maiwaya   Rikicin Masarautar kano ya na neman...

Shugabannin Kasuwar Kanti Kwari sun shiryawa Gwamnan Kano Addu’o’i na musamman

Daga jafar adam Shugaban kasuwar Kantin Kwari Sharu Abdullahi Namalam...

Dalilin Kwankwaso na kin shiga Hadakar ADC

Jam'iyyar NNPP ta ce abin da ya sa ba...