Da gudu zan karɓi tayin kujerar mataimakin shugaban ƙasa – Barau Jibrin

Date:

Daga Isa Ahmad Getso

Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Najeriya, Sanata Barau Jibrin ya ce da zaran shugaban ƙasa Bola Tinubu ya mika masa gayyatar zama mataimakinsa a zaben shekarar 2027 da gudu zai karɓa

Barau wanda ke ganawa da manema labarai a Abuja, ya ce a shirye yake ya sadaukar da kansa domin gudanar da duk wani aikin da shugaban ƙasar ya ba shi.

InShot 20250309 102512486
Talla

Sanatan wanda ya bayyana cewar ba ya buƙatar yin dogon jawabi dangane da lamarin a halin yanzu, ya ce lokaci bai yi ba da jama’a za su dinga tallata shi domin zama mataimakin shugaban ƙasa a zabe mai zuwa.

Barau ya ce bai ma san waɗannan ƙungiyoyin dake tallata shi ba, amma kuma ya buƙace su da su mayar da hankali wajen tallata ayyukan da shugaban ƙasa Tinubu ke yi da kuma goya masa baya.

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Sanatan ya ce da zaran lokacin siyasa ya yi, za su sadaukar da lokutan su domin tinkarar duk wani kalubale, yayin da ya ƙara da cewar yanzu lokaci ne na mulki amma ba na siyasa ba.

Jaridar Vanguard ta ce Barau ya bayyana Tinubu a matsayin shugaban da ya samar da ci gaba da dama a bangaren siyasa, ciki harda taimaka masa wajen komawa Majalisa da kuma zama mataimakin shugaban majalisar.

 

Saboda haka, Sanatan ya ce da zaran Tinubu ya ce masa ga aikin da yake so ya yi, a guje zai karɓa, kuma yana tabbatar da goyan bayan sa ɗari bisa ɗari ga shugaban.

A makwannin da suka gabata ne, baraka ta fito fili tsakanin ƴayan jam’iyyar APC mai mulki dangane da kujerar mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima a zabe mai zuwa.

Gwamnatin Kano ta bada hutun sabuwar shekarar Musulunci

Wannan ya haifar da ruɗani a taron da jiga jigan jam’iyyar suka gudanar a shiyar arewa maso gabas, wadda ta kai ga bai wa hammata iska.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Tun bayan lokacin ake rade radin cewar Tinubu zai sauya mataimakinsa Shettima a zabe mai zuwa, yayin da aka fara bayyana sunayen wasu fitattun ƴan siyasa daga ƴankin arewa maso yamma a matsayin waɗanda ake hasashen na iya samun kujerar.

Wata majiya kuma ta ce daga cikin masu neman kujerar a ƙarƙashin ƙasa har da wasu gwamnonin arewa maso gabas dake kammala wa’adin mulkin su a shekarar 2027.

Wasu daga cikin shugabannin jam’iyyar APC sun ce shugaba Tinubu ne kawai ke da hurumin zaben wanda zai mara masa baya, kuma hakan zai faru ne da zaran jam’iyyar ta tabbatar masa da kujerar takarar a taron zaben fidda gwanin da za’ayi.

Ya zuwa yanzu dai, ƴan siyasa da wasu jama’ar Najeriya na ci gaba da bayyana ra’ayoyin su dangane da wannan dambarwar wadda ake ganin ka iya raba kan jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Hukumar kula da almajirai ta Kasa ta kaddamar da yiwa almajirai Rijista a Kano

Daga Saminu Ibrahim Magashi   Hukumar kula da almajirai da yaran...

Inganta tsaro: Shugaban K/H Tarauni ya ba da fili domin gina ofishin Civil Defence a karkasara

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Shugaban karamar hukumar Tarauni, Alhaji Ahmed...

Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-nade

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nada Malam...

Gwamnatin Kano ta bada hutun sabuwar shekarar Musulunci

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga...