Kotu a Kano ta sami wani Tela da laifin takurawa makwabtansa da karar keken dinki

Date:

Wata kotu a Kano ta samu wani tela da laifin gurɓata muhalli da karan da kekensa ke yi.

Ma’aikatar kula da muhalli ta jihar ce ta kai ƙarar telan mai suna Mubarak Yusuf, kan yadda keken ɗinkinsa da kuma injin janareto ke damun mutanen anguwa da daddare.

InShot 20250309 102512486
Talla

Wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar, ta ce duk da cewa ya musanta zargin, amma ta gabatar da hujjoji da suka gamsar da kotun.

Har ila yau, kotun ta kai ziyarar gani da ido shagon da telan ya ke aiki, inda kuma ta tabbatar da cewa karan kekensa yana hana mutane barci da daddare, abin da ya saɓa wa sashi na 7 na dokar kare lafiyar al’umma ta 2019.

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

“Don haka ne kotun ta yanke hukuncin taƙaita masa lokutan yin aiki, inda yanzu zai riƙa aiki daga karfe 6:00 na safe zuwa 9:00 na dare,” in ji sanarwar.

Kwamishinan muhalli na jihar ta Kano, Dakta Dahir Hashim ya yaba wa kotun bisa wannan hukunci, inda ya ƙara nanata zimmar ma’aikatar na ganin ta tabbatar da cewa kowane mutum ko kuma wuraren kasuwanci sun bi matakan kare lafiyar al’ummar da kuma muhalli.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: Bam ya fashe a Kano ya hallaka wasu ya kuma jikkata wasu

Aƙalla mutum biyar ne aka tabbatar da rasuwarsu, yayin...

“BAMA YI”: Kalma mai alamta tsayuwar alkiyamar raggo ko mutakabirin dansiyasa – Dr. Murtala Iliyasu Ayagi

  Daga Dr. Murtala Iliyasu Ayagi malamin a Kwalejin Koyar...

2027: Tinubu ya bayyana lokacin da zai ambata sunan wanda zai yi masa mataimaki

I'mFadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai...

Ciyaman din Wudil ya kaddamar da aikin gina magudanan ruwa a wasu garuruwa a yankin

Daga Maryam Adamu Mustapha   Shugaban karamar hukumar Wudil, Hon. Abba...