Daga Rahama Umar Kwaru
Shugaban karamar hukumar wudil Hon. Abba Muhammad tukur Talban Makaman Kano ya ba da umarnin gyaran rijiyoyin burtsatse na tuka-tuka guda 100 a fadin karamar hukumar.
Hakan ya biyo bayan koke koken da al’ummar karamar hukumar wudil ke kan matsalar Ruwa, hakan tasa nan take Talban makama ya bada umarnin a kawu kayan gyara domin tunkarar wannan matsala, Kuma cikin ikon Allah kayan gyara sun iso, tuni an fara wannan aiki.

Hakan na kunshe ne cikin wata Sanarwa da mataimaki ga shugaban karamar hukumar wudil kan kafafen yada labarai Com. Abba Ashiru Utai ya aikowa Kadaura24.
Rikici: Dan Majalisar NNPP ya zargi Sanusi Bature da yi wa Gwamnan Kano zagon kasa
Ya ce matakin da Shugaban karamar hukumar zai taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalar karancin ruwan sha da ake fama da ita a yankin.
Sanarwar ta ce Abba Muhammad Tukur ya ba da Umarnin a kammala aikin ba tare da bata lokaci ba, saboda tuni duk kayan da za a yi aikin da su sun Isa karamar hukumar ta Wudil.
” Babu shakka a wannan karo za mu kawo karshen matsalar ruwan sha, kuma bayan kammala gyaran wadancan rijiyoyin burtsatsen za mu fara gina wasu sabbin rijiyoyin .