Daga Ibrahim Abubakar Diso
Tsohon Dan Majalisar wakilai da ya wakilci karamar hukumar Gwale Muhammad Bashir Hussari Galadanchi ya raba kudi da shanu ga Shugabannin jam’iyyar APC na Karamar hukumar .
Hon. Muhammad Bashir Hussari Galadanchi ya gwangwaje yan jam’iyyar APC da shanu har goma sha daya inda kowacce mazaba za ta rabauta da sa guda daya.

Su kuma shugabannin jam’iyya na karamar hukumar Gwale an ba su sa guda daya .
Haka zalika Hon. Hussari ya baiwa dattijan jam’iyya Naira miliyan daya da Dubu Dari shida (1.6), tsohon dan majalisar ya kuma ba da Naira dubu uku-uku ga yan jam’iyyar APC dubu uku dake karamar hukumar Gwale.
Kungiyar RATTAWU ta aike da ta’aziyyar mutane 22 yan wasan Kano da suka rasu
Kazalika Hon. Hussari ya rabawa yan social media na karamar hukumar Gwale dubu shida-shida .
Husari ya raba shanu Goma sha daya, inda kowanne shugaban APC na mazabun 11 za su sami guda.
Da yake bayyana sakon tsohon dan majalisar, shugaban jam’iyyar APC na Karamar hukumar Gwale Umar Yusuf Kashekwabo ya ce Hussari ya ba da tallafin ne domin tallafawa yan jam’iyyar don su yi bikin Sallah cikin nishadi.
” Muna yabawa wannan Hon. Hussari bisa Wannan kokarin da ya yi, kuma hakan ya nuna yana kimanta Shugabannin jam’iyyar APC, saboda cewa ya yi Shugabannin jam’iyyar yake so su raba kayan don su Isa ga wadanda ya kamata.