Al’ummar Kano ku baiwa AA Zaura hadin Kai domin ya kawo karshen fadan Daba – Baba Yawale

Date:

Daga Halima Umar Dogo

 

Babban Hadimin AA Zaura Alhaji Baba Yawale ya bayyana cewa tsohon Dan takarar Sanatan kano ta tsakiya a jam’iyyar APC Abdulssalam Abdulkareem wanda aka fi Sani da A A Zaura shi kadai ne mutum daya tilo a jihar Kano da ya ke taimakawa al’umma ba tare da neman wani mukamin gwamnati ba.

“Ya na kokarin baiwa ‘ya’yan talakawa fifiko wajen samar musu da rayuwa mai inganci, musamman wajen dakile fadan Daba da shan miyagun kwayoyi a fadin jihar Kano”.

IMG 20250415 WA0003
Talla

Alhaji Baba Yawale ya bayyana hakan ne a wata sanarwar da ya sanyawa hannu kuma ya aikowa Kadaura24.

Ya ce A A Zaura ya sadaukar da rayuwarsa wajen samar wa al’ummar jihar kano musamman matasa rayuwa mai kyau.

Kotun daukaka kara ta yanke hukunci kan zaben kananan hukumomin Kano

“Muna kira ga al’ummar Jihar Kano da su ba shi goyon baya wajen ganin ayyukan da yake yi don ci gaban Jiharmu ta Kano ya Sami nasarar da ake fata.

Idan za a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a Yan kwanakin nan bayan dawowar fadan daba a Kano , AA Zaura ya dage Yana ta tattaunawa da masu ruwa da tsakin domin ganin yadda za a kawo karshen fadan daba a fadin jihar Kano.

InShot 20250309 102403344

Da sauran Shugabannin al’umma a jihar Kano za su hada kai da A A Zaura da an sami nasarar kawo karshen fadan Daba da yaki ci yaki cinyewa a jihar Kano , musamman a kananan hukumomin dake kwaryar birnin jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Babbar Sallah: Gwamnatin Kano ta sanar da ranar rufe makarantu a jihar

Daga Rahama Umar Kwaru   Gwamnatin Jihar Kano ta bayar da...

Ban San Taulaci ba Sai da na Zama Sarkin Kano – Sarki Sanusi II

Daga Isa Ahmad Getso Sarkin Kano na 16 Muhammadu Sanusi...

Iftila:I: Gwamnatin Kano ta Aiyana Ranar Litinin a Matsayin Ranar Hutu

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin...

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta Kano ta zabi sabbin shugabanninta

Kungiyar shugabannin kafafen yada labarai ta jihar Kano ta...